Saturday, 25 March 2023

وفاة ‏السلف

*🛑 تاريـخ وفـاة عظمـاء الاسـلام الذيـن يكثـر السـؤال عنهـم :*

*📒 محمد صلى الله عليه وسلم 11 هجري*
📕 أبو بكر الصديق 13 هجري
📔 عمر بن الخطاب 23 هجري
📙 عثمان بن عفان 35 هجري
📘 علي بن أبي طالب 40 هجري
📗 عائشة بنت أبي بكر 57 هجري
📕 ابن عباس 68 هجري
📔 ابن عمر 73 هجري
📘 سعيد بن المسيب 94 هجري
📙 عمر بن عبد العزيز 101 هجري
📗 الحسن البصري 110 هجري
📕 أبو حنيفه 150هجري
📗 مالك بن أنس 179 هجريه
📘 الشافعي 204 هجري
📕 ابن راهويه 238 هجري
📙 أحمد بن حنبل 241 هجري
📗أحمد بن سعيد الدارمي 253 هجري
📘 عبد الله بن عبد الرحمن الدارمي 255 هجري
📔 البخاري 256 هجري
📕 مسلم 261 هجري
📗 ابن ماجه 273 هجري
📘 أبو داود 275 هجري
📙 الترمذي 279 هجري
📗عثمان بن سعيد الدارمي 280هجري
📔 النسائي 303 هجري
📕 ابن جرير الطبري 310 هجري
📘 ابن خزيمة 311 هجري
📕 ابن حبان 354 هجري
📙 الدارقطني 385 هجري
📔 الحاكم 405 هجري
📗 ابن حزم 456 هجري
📘 البيهقي 458 هجري
📕 ابن عبد البر 463 هجري
📔 الخطيب البغدادي 463 هجري
📗 ابن العربي 543 هجري 
📘 ابن رشد الحفيد 595 هجري
📙ابن الجوزي 597 هجري
📔 القرطبي صاحب تفسير الجامع لأحكام القرآن 671 هجري
📕النووي 676 هجري
📗 ابن تيمية 728 هجري
📔 الذهبي 748 هجري
📘 ابن القيم 751 هجري
📙 ابن كثير 774 هجري
📗 ابن رجب 795 هجري
📔 ابن حجر العسقلاني 852 هجري
📗 السيوطي 911 هجري
📘 الأمير الصنعاني 1182 هجري
📕محمد بن عبد الوهاب 1206 هجري
📗الشوكاني 1250 هجري
📔 الألوسي 1342 هجري
📙 ابن سعدي 1376 هجري
📕 الشنقيطي 1393 هجرة
📘ابن باز 1419 هجري
📗 الألباني 1420 هجري
📔 ابن عثيمين 1421 هجري

*⭕ .. أرسلها للطلاب ..*
*⭕ .. أرسلها لقروب أنت مشترك فيه  ..*
*💡ثقّف من حولك من هم عظماء الإسلام .*
*ــــــــــــــــــــــــــــــــــ*
📚  للاشتراك في *طَلَـبُ الْعِلْـمِ الشَّرْعِـيِّ* على:
⇜ *الواتس اب WhatsApp*
https://chat.whatsapp.com/It1rbLAmatWLeFc0YaX1gh
⇜ *التلي جرام Telegram*
https://t.me/fwaeeds

Wednesday, 4 January 2023

NISA'U AHLUL JANNAH (MATASA)

*🌳NISA'U AHLUL JANNAH🌳*

*🔷Matasa Mahangan Al'ummah🔷*

✍️ Haruna Isah Muhammad
hdindima@gmail.com

🔶قال حكيم: 

*💡«إذا أردت أن تعرف مستقبل أمة فانظر ماذا يفعل شبابها»*
🔷 Wani mai Hikima ya ce:

*💡«in kana son ka gane nan gaban al-Ummah (yaya zata kasance) , ka kalle me matasanta suke aikatawa a yanzu»*

📖 Faidodi Masu tarin Yawa

       *📻Bayani📻*

✔️Yan'uwana ba abun dake haskaka yaya al'ummah zaka kasance in ba matasanta ba, in kaga sun lalace to nan gaba sai gyaran Allah.

✔️Amma in har al'ummah ta tashi da gsk har matasa suka gyaru akwai tsammanin za'a samu al'ummah mai kyau.

✔️A yanzu fa an kai Uba yana aikan dansa ya sayo masa Kayan maye, ko kaga iyaye na gani yaransu na Rawa, na wake wake, ko kaga fitsara iri daban daban.!!!

✔️Allah ya wuce maba gaba, ya kuma gyara mana matasanmu baki daya. Ameeeeeen.
www.hdindima.blogspot.com

Monday, 2 January 2023

FAIDODI MASU TARIN YAWA (RIKO DA ALLAH)

*🔲 NISA'U AHLUL JANNAH*

🔷Riko da Allah

✍️ Haruna Isah Muh'd
hdindima@gmail.com

🔺 سئل إبراهيم بن أدهم، لم لا تخالط الناس؟ 

▪️فقال : *« إن صحبت من هو دوني أذاني بجهله، وإن صحبت من هو فوقي تكبر علي، وإن صحبت من مثلي حسدني (إلا من رحمه الله) ، فاشتغلت نمن ليس في صحبته ملل ولا في وصله انقطاع، ولا في الأنس به وحشة».*

🔺 Wata rana an tambayi Ibrahim Ibn Adham, wai shin me yasa baka son yawan Mu'amala da mutane sosai ne?

▪️ Sai ya ce *:« In har na matsi wanda na fishi sai ya cutar dani da Jahilcinsa, in kuma na matsi wanda yake sama dani sai ya dinga min Girman kai, in kuma na matsi wanda muke tsara dashi sai ya min Hassada (Sai wanda Allah ya tsamar kawai), dan haka shi yasa kawai na koma na damu da wanda in na matseshi ma ba wani zamewan da zanyi, haka kuma in na gyara alaqa dashi sam bata tsinkewa, haka kuma in ka kyautata alaqa dashi ba zai taba barinka kayi kewa ba (yana nufin Allah).»*

📒 Faidodi Masu tarin Yawa

       *♦️ Bayani ♦️*

✔️Wadan nan bayanai suna nuna mana ba yadda za ayi ka gamsar da mutane ko ka samu jin dadin tarayya da mutane 100%, dan haka in kana son ka samu jin dadi mai dorewa, ka koma zuwa ga Allah.

✔️Allah ya kara bamu ikon kyautata Alaqarmu dashi . Ameeeeeen.

www.hdindima.blogspot.com

Monday, 12 December 2022

FAIDODI MASU TARIN YAWA

*⭕ANNISA'U AHLUL JANNAH⭕*

*🔰FAIDODI MASU TARIN YAWA*
*_______________________*
✍️ Haruna Isah Muh'd
hdindima@gmail.com

♦️قال الإمام مالك رحمه الله:

*🔲«لن يصلح آخر هذه الأمة الا بما صلح به أولها»*

♦️ Imam Malik (Allah ya masa Rahama) ya ce:

*🔲  «Karshen wan nan Al'ummah ba zai taba gyaruwa ba, sai sun kama abun da ya gyara magabatansu»*

*_________________________*

          *⚪BAYANI⚪*

✔️Anan Imam Malik yana an karar damu ne, cewa Muddin muna son mu tsira dole sai mun yi irin abun da magabata suka yi na addini, mu iya kokari muke kwatantawa.

✔️Dan muddin ba muyi irin nasu ba kuma muna son lamurammu su gyaru irin nasu, tamkar muna yaudaran Kammu ne.

✔️Allah ya bamu ikon kwatanta abun da suka yi, irinsu *Amana*, *yawan Sallah*, *Zumunci*, *Taimakon Juna*, *Guje ma Shirka*, *da aikata duk wani abu maras kyau. Ameeeeen
*__________________________*

Thursday, 17 November 2022

SHIRIYAR AL-QURAN

*🔘AL-MAR-ATUSSALIHA ORPHANS AND VULNERABLE FOUNDATION🔘*

🔜 Shiriyar al-Quran ita ce shiriya

✍️ Haruna Isah Muh'd
hdindima@gmail.com
*___________________*

● *{يا أيها الذين آمنوا اذكروا الله ذكرا كثيرا * وسبحوه بكرة وأصيلا * هو الذي يصلي عليكم وملائكته ليخرجكم من الظلمات إلى النور وكان بالمؤمنين رحيما}*

⌛Allah (Swt) ya ce:

*«Ya ku wadan da kuka yi Imani, ku na zikrin Allah (ambatonsa) zikiri mai yawa, kuma kuna masa tasbihi safe da yamma@ Shi ne wanda yake yabonku da kuma Mala'ikunsa suna maku Addu'a, @ don ya fitar daku daga duhu (na Shirka) zuwa ga haske (na Imani)»*
*_______________________*

♦️ *«مَن صلَّى اللهُ تعالى عليه وملائكته فقد ‌أفلح ‌كل ‌الفلاح، وفاز كل الفوز، فهذه الصلاة منه تبارك وتعالى ومن ملائكته إنما هي سببٌ الإخراج لهم من الظلمات إلى النور، فأيُّ خيرٍ لم يحصل لهم، وأيُّ شرٍّ لم يندفع عنهم؟! فيا حسرة الغافلين عن ربهم؛ ماذا حُرِموا من خيره وفضله؟!»*

📜ابن القيم، الوابل الصيب (ص: 72)

♦️Ibn al-Kayyim ya ce game da wan nan Aya:

*«Tabbas duk wanda Allah ya yabeshi kuma Mala'ikunsa suka masa Addu'a wan nan ya rabauta, babban Rabo, kuma ya tsira, Yabon Allah da kuma Addu'ar Mala'ikunsa dalili ne na fitar da mutane daga Duhu zuwa ga Haske, akwai wani alkhairin da mutanen nan basu samu ba?!!  kuma shin akwai wani Sarrin da ba'a tsaresu dashi ba?!, Tabbas rafkanannu ga Ubangijinsu sun tafka asara (wadan da basa zikiri), sun san irin Alkhairi da Falalansa da aka haramta masu kuwa?! (Wato an hanasu babban Alkhairi , muddin basa zikiri)»*
*________________________*

🪞 قال النبي ﷺ :

*«(علام يقتل أحدكم أخاه ، إذا رأى أحدكم من أخيه ما يعجبه فليدع له بالبركة)»*

📜رواه ابن ماجة 3509 

🪞 Manzon Allah (saw) ya ce:

*«Alama ce da daya daga cikinku ke yakan Dan'uwansa dashi, idan dayanku yaga wani abu daga Dan'uwansa wanda ya burgeshi, ya masa Addu'a na albarka (Alkhairi)»*

Ibn Majah (3509)

❍ قال الشيخ ابن عثيمين رحمه الله :

● *«فإذا رأى الإنسان ما يعجبه وخاف من حسد العين فإنه يقول: ما شاء الله تبارك الله، حتى لا يصاب المشهود بالعين، وكذلك»*

❍ Sheikh Ibn Uthaimin (R) ya ce:

*« Idan dayanku yaga wani abun da ya burgeshi kuma yana tsoron Kambun baka, sai ya ce "Masha Allah, Tabarakallah" ta yadda ba abun da zai samu dayan daga Kambun baka»* 

*«Haka kuma idan mutum yaga abun da ya burgeshi daga Kudi ko Dukiyarsa sai ya ce " Masha Allah laa Kuwwata Illa billah" dan kada ya kwallafu da dukiyar har ta wuce iyaka a zuciyarsa , da zarar ya fadi Addu'ar tabbas ya jingina Lamarin zuwa ga wanda ya cancanta (wato ya jingina zuwa ga Allah)»*

▪️ *إذا رأى الإنسان ما يعجبه في ماله فليقل: ما شاء الله لا قوة إلا بالله؛ لِئَلاَّ يعجب بنفسه وتزهو به نفسه في هذا المال الذي أعجبه، فإذا قال: ما شاء الله لا قوة إلا بالله، فقد وكل الأمر إلى أهله تبارك وتعالى»*

📜فتاوى نور على الدرب الشريط رقم 297

*📸Bayani📸*

Yan'uwana musulmai har yanzu bamu makara ba, mu kama azkar wato zikirorin da manzon Allah ya karantar, kuma muna yinsu yadda ya koyar ba yadda wasu ke bata tsarin ba, zikiri abu ne na nutsuwa ba na hauka ba, 

Muna iya kokarimmu muna daukan wanda zamu dawwama muna yi, dan kadan daga cikin Rahamar da zamu samu ita ce, Allah da kansa zai yabemu kuma zai saka Mala'ikunsa su mana Addu'a. Wan nan kawai zai gwada mana girman Zikiri (wato ambaton Allah)

Zikiri ya hada da Karanta al-Quran da sauran Azkar na barci na safe da yamma, na tafiya , na shiga kasuwa, shiga Ban daki da fitarsa da sauransu................

Allah yasa mu dace baki daya. Ameeeeen
www.hdindima.blogspot.com

Sunday, 6 November 2022

HADITH CLASS 35

*🪞AL-MAR-ATUSSALIHA ORPHANS AND VULNERABLE FOUNDATION (ZAUREN MACE TA GARI DON TALLAFA WA MARAYU DA MARASSA GALIHU)🪞*

*🔰HADITH CLASS 25🔰*

✍️ Haruna Isah Muh'd
hdindima@gmail.com
*_______________________*

*🔲هجرة المرأة فراش زوجها🔲*

*♦️KAURACEWAR MACE GA SHINFIDAR MIJINTA♦️*

عن أبي هريرة رضي الله عنه قال: قال رسول الله صلى عليه وسلم

*_«إذا دعا الرجل امرأته إلى فراشه، فلم تأته ، فبات غضبان عليها، لعنتها الملائكة، حتى تصبح»_*

متفق عليه

🔘Hadith 001🔘

An karbo Hadith daga Abu Huraira (RA) ya ce, Manzon Allah (saw) ya ce:

*_« idan mutum ya kira matarsa zuwa ga shinfidarsa (don saduwa ta aure) sai Taki zuwa, har ya kwana yana fushi da ita, Mala'iku zasu la'anceta har ta wayi gari»_*

Bukhari da Muslim
*_________________________*

⚪Hadith 002⚪

عن ابن عمر رضي الله عنه،  أن رسول الله صلى عليه وسلم، قال، 

*_«لعن الله المسوفات، التي يدعوها زوجها الى فراشه، فتقول سوف حتى يغلبه عيناه»_*

الطبراني

☑️An karbo Hadith daga dan Umar (Abdullahi dan Umar) (RA) ya ce: lallai Manzon Allah (saw) ya ce:

*_« Allah ya la'anci (ya tsine) wa macen da take cewa jirani ina zuwa, wacce idan mijinta ya kirata zuwa ga shinfidarsa (don saduwar Aure) sai ta ce masa, jirani ina zuwa, har idonsa ya rinjayeshi (har barci ya daukeshi»_*

Dabarani

*________________________*

*🔘Hadith 003🔘*

عن أبي هريرة رضي الله عنه، أن رسول الله صلى عليه وسلم قال: 

«لعن الله المفسلة، التي إذا أراد زوجها أن يأتيها قالت أنا حائض»

أبو يعلى في مسنده

☑️An karbo Hadith daga Abu Huraira (RA) ya ce: lallai Manzon Allah (saw) ya ce: 

*_«Allah ya la'anci mai kashe shaawar mijinta da ganganci, wacce  idan mijinta ya nufeta da saduwa ta aure sai ta ce, ina Al-adah ( kuma na karya)»_*

Abu Yaalah
*________________________*

🔲BAYANI🔲

Yan'uwa mu kara kiyayewa ga yadda zamantakewarmu ke gudana, lura da hadithai din nan, suna daga cikin abubuwan da suke kawo matsalolin aure, sama da tunanin kowa, 

Dan haka mu iya kokarinmu don kyautata zamantakewa. 

Kuma gareku maza, dan an fadi haka, ba lasisi ba ne namiji ya cutar da matarsa, yadda muke shaawa suma haka ne, kuma Allah ya ce « suma mata suna son irin abun da muma muke so, duk wanda ya take hakkinta na shaawa ko na biyan bukata shima yana da irin tasa azabar da zai tarar.

Allah ya tsaremu baki daya. 
➖➖➖➖➖➖➖

Tuesday, 25 October 2022

HANYAR SAMUN ALJANNAH CIKIN SAUKI

🌻AL-MAR-ATUSSALIHA ORPHANS AND VULNERABLE FOUNDATION (ZAUREN MACE TA GARI DON TALLAFA WA MARAYU DA MARASSA GALIHU)🌻

🌱HANYAR SAMUN ALJANNAH CIKIN SAUKI🌱

✍️ Haruna Isah Muh'd
hdindima@gmail.com

♦️قال رسول الله صلى عليه وسلم:

«من ذب عن لحم أخيه بالغيبة، كان حقا على الله أن يعتقه من النار»
                        رواه أحمد

♦️Manzon Allah (saw) ya ce:

«duk wanda ya ba da kariya ga naman dan'uwansa daga gulma (wato wanda ya hana ayi gulman wani), ya zama hakki akan Allah zai 'yantashi ga barin shiga wuta (ba zai shiga wuta ba)»

Ahmad ne ya Rawaito

🔘BAYANI🔘

Yan'uwana gulma illa ce, tamkar ka saka mutum ne a gabanka bayan ya mutu kana yankan naman jikinsa kana ci.

Allah ya yi hani akan gulma, kuma duk wanda ya yi kokarin rabuwa da gulma ya kuma hana wasu yin gulma, Allah ya yi alkawa ma kamsa, zai 'yanta mutumin nan daga shiga wuta.

Allah ya kara bamu ikon binsa yadda ya kamata. Ameeeeen

🖥️FOR MORE🖥️
www.hdindima.blogspot.com