Monday, 10 June 2019

MADACI BISHIYA MAI AMFANI AMMA SAI DACI

*MADACI WANI BISHIYA NE MAI DACIN GASKE, AMMA KUMA YANA MAGANI, AMMA GA WANI WAI SUNANSA MADACI!!!*
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
✍ Haruna I Muh'd
*080 6958 2878*
Hdindima@yahoo.com
🌹🌹🌹🌹🌹🌹

Yan'uwana ku biyoni a hankali kuji hirata da Madaci.

Turkashi!! Jiya an kwalla rana matuka kuma sai gashi kafin yamma an samu ruwa, ikon Allah, nazo wucewa kenan sai na tarar da Madaci yana zaune a majalisa shi kadai, kuma abun mamaki yana cikin rana!!

*NI*: Madaci mai ke faruwa ne haka yau na ganka kamar an koroka daga gida ko baka da kudin cefane ne?!!

*MADACI*: Ka fara kenan ko, kai ko ma kaji me ke damuna baka yi ba, kawai ka hau kaina da zancen gida, gida kam ai sai wanda Allah ya bashi mata ta gari, amma in ba haka ba zaka ga yana yawo yana lissafi akan titi.

*NI*: kai madaci so kake dai sai na zauna, ni kuma yau so nake in je in karbo bashina dan naji anyi salary, sabo da masu karban salary wani lokaci ma ko isansu baya yi, kasata kenan!.

*MADACI*: Hahahahaha ai ni na riga na karbo nawa, kai ne ka makara, amma fatana kar kaje a hanya kaga kaga _Direrriya_ kaima ka nemi cikin rana ka zauna irina.

*NI*: Kai Madaci nifa ban gane ina ka dosa ba, so dai kake sai na zauna, kuma a rana, amma dan ka bani labari bari in zauna na minti uku. Amma ban gane direrriya ba!!, kana nufin zanga wata mata ta diro a KEKE NAPEP ne?

*MADACI*: Hahahahaha, abokina kenan, ni ko labari ma ba zan baka ba.

*---------------*
Sai muka zauna shiru kowa na zuwa ma kowa ido
*---------------*
*NI*: Kai ka ganka ko daman na fada maka bata min lokaci kawai zaka yi, amma sai naga kamar Zikiri Madaci yake yi, yana Astagfirul-Lah, kai sai na lura da kyau naga kamar yana son ya kawo wata aya ce a cikin al-Qur'an. Sai na ce kai Madaci me kake tattaunawa kai kadai?!.

*MADACI*: Na kasa kawo wata aya ce ta al-Qur'an, amma zan iya tuna kan gaban da zan fada maka, in kaga dama ka dauka in kuma baka so ka kama hanyarka, Allah ya kiyaye dan ban san ina zaka isa ba.

*NI*: ko zaka iya tuna sakon ayar in tuna maka?

*MADACI*: EE tana maga ne akan _Jalabib_

*NI*: Hahahahaha na ganoka ga ayar

Surah Al-Ahzab, Verse 59:

*"يَا أَيُّهَا النَّبِيُّ قُل لِّأَزْوَاجِكَ وَبَنَاتِكَ وَنِسَاءِ الْمُؤْمِنِينَ يُدْنِينَ عَلَيْهِنَّ مِن جَلَابِيبِهِنَّ ذَٰلِكَ أَدْنَىٰ أَن يُعْرَفْنَ فَلَا يُؤْذَيْنَ وَكَانَ اللَّهُ غَفُورًا رَّحِيمًا"*

"O Prophet! say to your wives and your daughters and the women of the believers that they let down upon them their over-garments; this will be more proper, that they may be known, and thus they will not be given trouble; and Allah is Forgiving, Merciful."

*MADACI*: yauwa na tuna wan nan ayar ce, Amma sakona ita ce, sai kuma wan nan Sallah naga mafi Yawancin yan matanmu ba adon da suke yi kamar adon GYALE, ni kuma a ganina yawancin gyalen bai rufe dukkan jikinsu, kuma abun tausayimma har da yaran malamai, kai kusan ko ina fitinar ta shiga.

*NI*: har kasa jikina yayi saniyi duk da yadda Allah yake hana mata bude jiki amma yanzu ya fara zama kamar ma ba komai ba ne.!! Allah sarki al-Ummahta!!!!.

*MADACI*: tashi ka tafi nasan ka gane me nake nufi da direrriya, ai duk macen da tasa kaya amma duk zanen halittanta ya bayyana ina ji mana tsoron kar mu fada cikin wadan da ba zasu shiga al-Jannah ba, ko kamshinta ma ba zasu ji ba. (Kasiyatun Ariyat). Inji Manzon Allah (saw).

*NI*: Lallai Madaci abun da ka fada Gsky ce Allah ya bamu ikon gyrawa.

*MADACI*: Abokina kenan bamu makara ba, mu tura wan nan sako ma kowa, amma daci gareta kamar yadda Ni madaci nake da daci.

🌺🌺🌺🌺🌺🌺
www.hdindima.blogspot.com

No comments:

Post a Comment