*_MARABA DA BABBAN BAKO RAMADAN_*
🌿🌿🌿🌿🌿🌿
🌿🌿 0007 🌿🌿
————————
*_By Haruna I Muh'd_*
*_08069582878_*
*_hdindima.blogspot.com_*
———————
*FALALAR AZUMI*
———(D)———
10. *Allah ya tanada wa masu azumi gida ta musamman a Al-Jannah, yana da kofa mai suna _RAYYAN_ hakan ya fito ne daga bakin manzon Allah (saw) ya ce:*
*_"إن في الجنة بابا يقال له :الريان، يدخل منه الصائمون يوم القيامة، لا يدخل منه غيرهم، فإذا دخل آخرهم أغلق فلم يدخل منه أحد"_*
*_"Lallai a Al-Jannah akwai wani kofa ana kiransa RAYYAN takofar yan' Al-Jannah masu azumi zasu shiga a ranar al-Qiyamah, ba mai shiga (ta kofar nan) in basu ba, idan na karshensu ya shiga sai a rufe ba wanda kuwa zai sake shiga(ta wannan Kofa na masu azumi) "_*
11. *_Azumi na daga abubuwa na farko da suke kai mutum Al-Jannah,*
*Manzon Allah (saw) wata rana ya tara Sahabbai yana Tambayarsu kamar haka:_*
*_" من أصبح اليوم منكم صائما؟"_*
*_"Waye daga cikinku yau ya wayi gari yana Azumi?"_*
*Sayyidina Abu-Bakr ya ce: "Ni ya manzon Allah (saw)"*
*_"فمن اتبع منكم اليومة جنازة"_*
*_"Waye daga cikinku kuma yau ya raka gawa har Makabarta? "_*
*Sayyidina Abu-Bakr ya ce: "Ni ya manzon Allah (saw)"*
*_" فمن أطعم منكم اليوم مسكينا؟"_*
*_"Waye daga cikinku yau ya ciyar da miskini(Talaka)?"_*
*Sayyidina Abu-Bakr ya ce: "Ni ya manzon Allah (saw)"*
*_"فمن عاد منكم اليوم مريضا؟"_*
*_"Waye daga cikinku ya gaishe da maras Lafiya a yau?"_*
*Sayyidina Abu-Bakr ya ce: "Ni ya manzon Allah (saw)"*
*A karshe sai manxon Allah ya ce:*
*_"ما جتمعن في امرئ إلا دخل الجنة"_*
*_"Ba wanda zai hada wadan nan siffofi face sai ya shiga Al-Jannah "_*
12. *Azumi na kankare zunubai baki daya na bawa,*
*Manzon Allah (saw) ya ce :*
*_"فتنة الرجل في أهله، و ماله، و ولده، و جاره، تكفرها : الصلاة و الصوم والصدقة، والأمر، و النهي"_*
*_" Idan Allah ya jarrabi mutun akan Iyalansa, ko akan dukiyarsa, ko akan Yaransa, ko akan makobtansa, Abun da zai kankare masa zunubansa shi ne: Sallah, Azumi, Sadaka, yin umarni da kyakkyawan aiki da kuma hani kan munanan aiki"_*
*Allah yasa da wan nan yar nasiha ta zamu amfana baki daya, Allah ya kara bamu ladansa Ameeeeeeeeeeeen*
——N.B.——
*U CAN SHARE THIS FISABILIL-LAH*
——————
Via
*_hdindima.blogspot.com_*
No comments:
Post a Comment