*֮֮֮R֮֮֮A֮֮֮M֮֮֮A֮֮֮D֮֮֮A֮֮֮N֮֮֮ K֮֮֮A֮֮֮R֮֮֮E֮֮֮E֮֮֮M֮֮֮ 2֮֮֮0֮֮֮1֮֮֮9֮֮֮*֮֮֮
🌳🌳🌳🌳🌳🌳
*֮֮֮M֮֮֮u֮֮֮h֮֮֮i֮֮֮m֮֮֮m֮֮֮a֮֮֮n֮֮֮c֮֮֮i֮֮֮n֮֮֮ A֮֮֮z֮֮֮u֮֮֮m֮֮֮i֮֮֮*֮֮֮
🌳🌳🌳🌳🌳🌳
֮✍֮ *֮H֮a֮r֮u֮n֮a֮ I֮ M֮u֮h֮'֮d֮*֮
֮*֮0֮8֮0֮ 6֮9֮5֮8֮2֮8֮7֮8֮*֮
Hdindima@gmail.com
☂☂☂☂☂☂
Bismillahir-Rahmanir-Raheeem
🌻🌻🌻🌻🌻🌻
Yan'uwana musulmai lallai watan Ramadana yana da falala sosai tare da muhimmanci a rayuwarmu tanan Duniya da kuma Lahira.
Ga kadan daga cikin Falala da muhimmancin Azumin:
1. Allah (swt) ya farlanta wan nan Azumi a kammu da kuma al-Ummah da ta rigayemu.
(Qur'an:2:183)
2. Sanadiyar Azumi Allah yana gafarta wa mutane duk zunubansu, kamar yadda Manzon Allah ya ce " Wanda yayi Azumin watan Ramadan yana mai Imani da kuma sa ran samun Lada, za a gafarta masa duk abun da ya aikata a baya"
3. A Azumi ne Allah ya gwada mana cewa ladansa ba adadi, kawai Ladan kamfata za a yi a bashi.
Manzon Allah ya ce: " Allah ya ce duk ayyukan bayi sakamakonsa nasu ne, amma banda Azumi ita kam tawa ce, kuma Ni zan ba da ladansa,....."
A karkashin wan nan Hadith Allah ya ambato abubuwa masu muhimmanci kan wan nan Wata mai al-Barka:
a) Allah ya ware Azumi ya zama nashi ne dan yana cewa "bawana yabar ci da sha da kuma sha'awarsa duk danni" ni zan bashi ladan hakan.
b) Allah fa da kansa ya ce zai saka ma wadan ya yayi Azumi, dan ya gwada karrama mai Azumi.
c) Allah ya ce Azumi garkuwa ce, zata hana mutum aikata munanan ayyuka, kuma manzon Allah ya ce
:" Azumi garkuwa ce wada ake samu tsanin mutum da shiga wuta".
d) Kuma a Hadith din Allah ya ce warin da yake fita daga bakin mai Azumi darajarsa yafi kamshin Turaren Al-Misk, hakan na gwada yadda Allah yaba Azumi daraja.
e) Allah ya ce mai Azumi zai yi farin-ciki a wurare biyu,
i. Lokacin da yayi bude baki da kuma
ii. Lokacin da zai hadu da Ubangiji, dan zai samu lada mai yawa.
4. Azumi zai ceci mai yinsa a ranar al-Qiyamah, Manzon Allah (saw) ya ce :" Azumi da al-Qur'an zasu ceci bawa ranar al-Qiyamah, Azumi zata ce ya Allah na hanashi cin komai da kuma sha'awarsa, ka bani cetonsa mana! Sai Al-Qur'an ma ya ce ya Allah na hanashi Barci da dare, ya Allah ka bani cetonsa mana! (Sai manzon Allah) ya ce sai kuma a basu ceton".
Anan zamu takaita Allah ya bamu ikon fara Azumi lafiya ya sa mu gama lafiya ya kuma bamu duk ladan da ake samun a wan nan wata mai al-Barka.
Dan samun wan nan lada tun daga yanzu ka/ki tura wan nan sako grp naku dan muyi tarayya a ladan baki daya.
🌼🌼🌼🌼🌼🌼