Saturday, 11 May 2019

DARUSAN RAMADAN (002)

RAMADAN KAREEEM 2019
🌻🌻🌻🌻🌻🌻

MUHIMMANCIN KO FALALAR WATAN RAMADAN (02)
🌻🌻🌻🌻🌻🌻

✍ Haruna I Muh'd
    080 69582878
Hdindima@gmail.com
🌼🌼🌼🌼🌼🌼

Assalamu Alaikum yan'uwana maza da mata hakika Manzon Allah (saw) ya fada mana Falalar wan nan wata mai al-Barka.
–––––––

Yau zamu yi nazari ne akan Hadith guda daya mai tarin Darusa.
👇👇👇👇👇👇

Imam Ahmad ya fidda Hadith daga Abu Hurairah (RA) ya ce: Manzon Allah (SAW) Ya ce:

" An ba wa Al-Ummahta wasu al'amura guda biyar wadan da baa ba wata al-Ummah da tazo a baya ba, a cikin watan Ramadan:

👉 1. Warin da yake fita a bakin mai Azumi (darajarsa) yafi kamshin Turaren almisk a wajen Allah

👉 2. Mala'iku suna nema musu gafar Zunubansu har sai lokacin da suka yi buda-baki

👉 3. A ko wace rana kuma Allah yana kawata Al-Jannah yana kuma cewa :" saura kadan bayina su zo su sameni, (sun kusa su bar hidindimun duniya da cutarwar da suke tararwa wajen bin Allah)

👉 4. Kuma za'a daure Shaidanu daga ko wace zirga-zirga, ba su isa su cimma wadan da suke so su cimma ba a cikin bayin Allah na gari

👉 5. Kuma Allah zai gafarta musu a ko wace karshen dare, sai Sahabbai suka ce ya Manzon Allah ko ita ce Lailatul-Qadr? Sai ya ce ah-ah, ko wani mai aiki za a bashi ladan aikinsa ne da zarar ya gama aikinsa"

Imam Bazzar da Baihaqi ne suka rawaito a Kitab Thawab, Isnad nashi yana da rauni sosai, amma sashinsa akwai Shawahid Ingantattu.
––––––––

Allah ya bamu ikon cin moriyar da ke cikin an nan wata mai al-Barka.

🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
Visit our site:
www.hdindima.blogspot.com
🌲🌲🌲🌲🌲🌲🌲

No comments:

Post a Comment