Monday, 12 June 2017

RAMADAN MUBARAK (16)

*MARABA DA BABBAN BAKO RAMADAN*

🌿🌿🌿🌿🌿🌿
🌿🌿 *0016*🌿🌿
————————
*By Haruna I Muh'd*
*08069582878*
*hdindima.blogspot.com*

*———————*
*SHUGABAN ISTIGFARI*
*———————*

*Akwai babbar addu'ar da Manzon Allah ya kirata da shugaban Istigfari, wannan addu'a, manzon Allah (saw) ya ce :"duk wanda ya karantata da safe da zai mutu a ranar sakamakonsa Al-Jannah, haka in ya karanta da yamma da zai mutu a daren Allah zai bashi Al-Jannah "*

*Ga shugaban Istigfari kamar haka:*

*_"ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺃﻧﺖ ﺭﺑﻲ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺃﻧﺖ ﺧﻠﻘﺘﻨﻲ ﻭﺃﻧﺎ ﻋﺒﺪﻙ ﻭﺃﻧﺎ ﻋﻠﻰ ﻋﻬﺪﻙ ﻭﻭﻋﺪﻙ ﻣﺎ ﺍﺳﺘﻄﻌﺖ ﺃﻋﻮﺫ ﺑﻚ ﻣﻦ ﺷﺮ ﻣﺎ ﺻﻨﻌﺖ ﺃﺑﻮﺀ ﻟﻚ ﺑﻨﻌﻤﺘﻚ ﻋﻠﻲ ﻭﺃﺑﻮﺀ ﻟﻚ ﺑﺬﻧﺒﻲ ﻓﺎﻏﻔﺮ ﻟﻲ ﻓﺈﻧﻪ ﻻ ﻳﻐﻔﺮ ﺍﻟﺬﻧﻮﺏ ﺇﻻ ﺃﻧﺖ"_*

*_" Allhummah anta Rabbi La Ilaha illa Anta, khalaqtani wa ana abduka, wa Ana ala Ahdika, wa Wa'adika Mastada'atu, A'uzu bika min sharri ma Swana'atu, Abu'u laka bi'Ni'amatika Alayya, wa abu'u laka bi Zanbi, Fagfirli, Fa' innahu la Yagfiruz-Zunuba illa Anta"_*

   *Allah yasa da wan nan yar nasiha ta zamu amfana baki daya, Allah ya kara bamu ladansa Ameeeeeeeeeeeen*

——N.B.——
*U CAN SHARE THIS FISABILIL-LAH*
*————————*
*_"Kuyi gaggawa zuwa ga samun rahamar Ubangijinku, da kuma neman Al-Jannah, wacce fadin cikinta kamar fadin sama da kasa, an tanadeta ne kawai ga masu tsoron Allah"_*
——————

Via
*hdindima.blogspot.com*

Friday, 9 June 2017

RAMADAN MUBARAK (14)

*MARABA DA BABBAN BAKO RAMADAN*

🌿🌿🌿🌿🌿🌿
🌿🌿 *0014*🌿🌿
————————
*By Haruna I Muh'd*
*08069582878*
*hdindima.blogspot.com*

*———————*
*_ABUN DA MAI AZUMI AKE SO YAYI KENAN NA SUNNONIN MANZON ALLAH (SAW)_*
*———(D)———*

*Assalamu Alaikum*

   *Yan'uwana musulmai a cikin azumi akwai sunnonin manzon Allah da dama da ake son ko wani mai azumi ya dinga yinsu, ga kadan daga ciki kamar haka:*

*10*. *Yi Itikafi a masallaci, Manzon Allah (saw) ya kasan ce a ko wani goman karshe na Ramadan yakan tare masallaci don Ibada, lokacin da ya kusan rasuwa ma yakan yi Itikafi na kwanaki Ashirin*

*11* *Neman Daren Lailatul Qadr, ko wani musulmi ana son ya dage da neman daren Nan a goma na karshen Ramadan*
     *Manzon Allah (saw) ya ce:*

*_"تحروا ليلة القدر في الوتر من العشر الآواخر من رمضان"_*

*_"Ku nemi samun daren Lailatul Qadr a goman karshe na Ramadan ciki wuturi( tan 21st or 23rd or 25th or 27th or 29th)"_*

*Matar Manzon Allah kuma Uwar Muminai Nana Aishat ta tambayi Manzon Allah kan wani addu'a zata yi in ta samu ganin daren Lailatul Qadr? Sai ya ce:"*

*_"قولي: اللهم إنك عفو تحب العفو فاعف عني"_*

*_"Ki ce : Allahummah innaka Afuwwun tuhibbul Afwa fa'afu anni"_*

*Alamun Daren ya samu, shi ne Washe-gari rana in ta fito ba zata yi zafi sosai ba,*

*MUHIMMANCIN DAREN LAILATUL QADR*

*Lallai ba shakka muhimmancin daren na da dama, amma mafi muhimmancin shi ne,:*
*1. A daren aka saukar da al-Qur'an.*
*2. A daren ne Allah yake budget na shekara mai zuwa.*
*3. Ibadah a daren Lailatul Qadr yafi lada sama da wanda yayi ibada na watanni Dubu (80yrs).*
*4. Allah yayi rantsuwa da wan nan dare mai albarka.* ds

Surah Al-Qadr,
Verse 1:

*_"إِنَّا أَنزَلْنَاهُ فِي لَيْلَةِ الْقَدْرِ"_*

*_"Surely We revealed it on the grand night."_*

Verse 2:

*_"وَمَا أَدْرَاكَ مَا لَيْلَةُ الْقَدْرِ"_*

*_"And what will make you comprehend what the grand night"_*

Verse 3:

*_"لَيْلَةُ الْقَدْرِ خَيْرٌ مِّنْ أَلْفِ شَهْرٍ"_*

*_"The grand night is better than a thousand months."_*

Verse 4:

*_"تَنَزَّلُ الْمَلَائِكَةُ وَالرُّوحُ فِيهَا بِإِذْنِ رَبِّهِم مِّن كُلِّ أَمْرٍ"_*

*_"The angels and Jibreel descend in it by the permission of their Lord for every affair,"_*

Verse 5:

*_"سَلَامٌ هِيَ حَتَّىٰ مَطْلَعِ الفجر"_*

*_"Peace! it is till the break of the morning."_*

N.B
*Wasu na yada wai zaka ga cikin dare bishiyoyi sun kwanta daga gidanku sai ka hango dakin Kaabah, ko wai zaka ga duk gidaje an shafesu...... Irin wan nan ba gaskiya bane Allah ya bamu ikon Samun wan nan dare mai albarka*

   *Allah yasa da wan nan yar nasiha ta zamu amfana baki daya, Allah ya kara bamu ladansa Ameeeeeeeeeeeen*

——N.B.——
*U CAN SHARE THIS FISABILIL-LAH*
*————————*
*_"Kuyi gaggawa zuwa ga samun rahamar Ubangijinku, da kuma neman Al-Jannah, wacce fadin cikinta kamar fadin sama da kasa, an tanadeta ne kawai ga masu tsoron Allah"_*
——————

Via
*hdindima.blogspot.com*

Wednesday, 7 June 2017

RAMADAN MUBARAK (13)

*MARABA DA BABBAN BAKO RAMADAN*

🌿🌿🌿🌿🌿🌿
🌿🌿 *0013*🌿🌿
————————
*By Haruna I Muh'd*
*08069582878*
*hdindima.blogspot.com*

*———————*
*_ABUN DA MAI AZUMI AKE SO YAYI KENAN NA SUNNONIN MANZON ALLAH (SAW)_*
*———(C)———*

*Assalamu Alaikum*

   *Yan'uwana musulmai a cikin azumi akwai sunnonin manzon Allah da dama da ake son ko wani mai azumi ya dinga yinsu, ga kadan daga ciki kamar haka:*

*7* *Yawan yin sadaka a cikin Ramadana da wajen Ramadan*
        *Ya zo a Hadith Manzon Allah (Saw) ya kan zama mafi yawan ba da kyauta da sadaka a Ramadan, musamman lokacin da Mala'ika Jibril ya zo ya masa bitan al-Qur'an, yakan ninka kyautan da yake yi (saw)*

*8* *Yawan karanta al-Qur'an, wato ba lallai sai mahaddata ba, ko sura daya ka iya kayi ta mai-maitata Allah zai ninka maka lada akan hakan, dan Allah ya ce mana a wannan wata ta Ramadan Allah ya saukar da al-Qur'an wa Manzon Allah (saw)*
       *Allah ya ce:*

Surah Al-Baqara, Verse 185:

*_"شَهْرُ رَمَضَانَ الَّذِي أُنزِلَ فِيهِ الْقُرْآنُ هُدًى لِّلنَّاسِ وَبَيِّنَاتٍ مِّنَ الْهُدَىٰ وَالْفُرْقَانِ فَمَن شَهِدَ مِنكُمُ الشَّهْرَ فَلْيَصُمْهُ وَمَن كَانَ مَرِيضًا أَوْ عَلَىٰ سَفَرٍ فَعِدَّةٌ مِّنْ أَيَّامٍ أُخَرَ يُرِيدُ اللَّهُ بِكُمُ الْيُسْرَ وَلَا يُرِيدُ بِكُمُ الْعُسْرَ وَلِتُكْمِلُوا الْعِدَّةَ وَلِتُكَبِّرُوا اللَّهَ عَلَىٰ مَا هَدَاكُمْ وَلَعَلَّكُمْ تَشْكُرُونَ"_*

*_"The month of Ramazan is that in which the Quran was revealed, a guidance to men and clear proofs of the guidance and the distinction; therefore whoever of you is present in the month, he shall fast therein, and whoever is sick or upon a journey, then (he shall fast) a (like) number of other days; Allah desires ease for you, and He does not desire for you difficulty, and (He desires) that you should complete the number and that you should exalt the greatness of Allah for His having guided you and that you may give thanks."_*

*9* *Kiyamul Lail (Sallar Asham, ko Tahajjud ko sauran Nafiloli)*
       *A kan wan nan manzon Allah yana jan hankalinmu da mu dage da sallar Dare a ramadana da bayanta in da hali. Manzon Allah ya ce:*

*_"من قام رمضان  إيمانا واحتسابا، غفر له ما تقدم من ذنبه"_*

*_"Duk wanda yayi sallah (Asham ko Tahajjud ko Nafiloli na daban) a Ramadan, yana mai Imani da kuma tsammanin Samun lada (da sakamako mai kyau) a wajen Allah, za'a gafarta masa Zunubansa kaf da yayi a baya"_*

   *Allah yasa da wan nan yar nasiha ta zamu amfana baki daya, Allah ya kara bamu ladansa Ameeeeeeeeeeeen*

——N.B.——
*U CAN SHARE THIS FISABILIL-LAH*

*_"Kuyi gaggawa zuwa ga samun rahamar Ubangijinku, da kuma neman Al-Jannah, wacce fadin cikinta kamar fadin sama da kasa, an tanadeta ne kawai ga masu tsoron Allah"_*
——————

Via
*hdindima.blogspot.com*

RAMADAN MUBARAK (12)

*MARABA DA BABBAN BAKO RAMADAN*

🌿🌿🌿🌿🌿🌿
🌿🌿 *0012*🌿🌿
————————
*By Haruna I Muh'd*
*08069582878*
*hdindima.blogspot.com*

*———————*
*_ABUN DA MAI AZUMI AKE SO YAYI KENAN NA SUNNONIN MANZON ALLAH (SAW)_*
*———(B)———*

*4.* *Jinkirta yin sahur*
     *lallai ya tabbata daga Manzon Allah (saw) ya ce:*

*_"تسحروا فإن في السحور بركة"_*

*_"Ku yi sahur sabo da cikinsa akwai albarka "_*

*5.* *Kame Baki da duk kan gabbai akan abubuwan da Allah ya haramta*
     *Manzon Allah (saw) ya ce:*

*_" من لم يدع قول الزور والعمل به والجهل، فليس لله حاجة في أن يدع طعامه وشرابه"_*

*_"Duk wanda bai bar shaidar Zur ba( shaidar karya), ko amfani da ita, ko aikin jahilci (a Azumi) ba ruwan Allah ko ya bar cin abu ko shan abu, (ko yayi azubi ko kar yayi ba ruwan Allah)"_*

*6* *Ciyar da mai Azumi a watan Ramadan*
      *Manzon Allah (saw) ya ce :*
       *_"من فطر صائما فله مثل أجره، غير أنه لا ينقص من أجر الصائم شيء"_*

*_"Duk wanda ya ciyar da mai azumi (da abun bude-baki), yana da irin ladan mai azumin, ba tare da an rage na mai azumin komai ba"_*

   *Allah yasa da wan nan yar nasiha ta zamu amfana baki daya, Allah ya kara bamu ladansa Ameeeeeeeeeeeen*

——N.B.——
*U CAN SHARE THIS FISABILIL-LAH*
——————

Via
*hdindima.blogspot.com*

RAMADAN MUBARAK (11)

*MARABA DA BABBAN BAKO RAMADAN*

🌿🌿🌿🌿🌿🌿
🌿🌿 *0011*🌿🌿
————————
*By Haruna I Muh'd*
*08069582878*
*hdindima.blogspot.com*

*———————*
*_ABUN DA MAI AZUMI AKE SO YAYI KENAN NA SUNNONIN MANZON ALLAH (SAW)_*
*———(A)———*

*Assalamu Alaikum*

   *Yan'uwana musulmai a cikin azumi akwai sunnonin manzon Allah da dama da ake son ko wani mai azumi ya dinga yinsu, ga kadan daga ciki kamar haka:*

*1* *Gaggauta shan ruwa da zarar an tabbatar rana ta fadi*

*Manzon Allah (saw) ya ce:*

*_"لا يزال الناس بخير ما أجلوا الفطر"_*

*_"Mutane ba zasu gushe ba suna tare da al-khairi, matukar suna gaggauta shan ruwa"_*

*2* *Fara bude-baki da danyen kayan itatuwa ko dabino ko ruwa*

*_"Sahabin manzon Allah Anas (ra) ya ce manzon Allah ya kasance yana bude-baki da danyen abu, in babu ko da dabino ko da ruwa"_*

*3* *Yin addu'a lokacin bude baki*

*Sahabin manzon Allah, Abdul-Lahi ibn Umar ya ce manzon Allah in yazo bude-baki yakan karanta wan nan addu'a kamar haka:*

*ADDU'AR BUDE-BAKI(SHAN RUWA)*

*_"ذهب الظمأ وابتلت العروق وثبت الأجر إن شاء الله"_*

*_"Zhabaz-Zhama'u, Wabtallatil-Uruqu, Wathabatal-Ajru insha Allah"_*

   *Allah yasa da wan nan yar nasiha ta zamu amfana baki daya, Allah ya kara bamu ladansa Ameeeeeeeeeeeen*

——N.B.——
*U CAN SHARE THIS FISABILIL-LAH*
——————

Via
*hdindima.blogspot.com*

RAMADAN MUBARAK (10)

*MARABA DA BABBAN BAKO RAMADAN*

🌿🌿🌿🌿🌿🌿
🌿🌿 *0010*🌿🌿
————————
*By Haruna I Muh'd*
*08069582878*
*hdindima.blogspot.com*

———————
*FALALAR AZUMI*
———(G)———

19. *Duk wan da ya mutu yana Azumi zai shiga Al-Jannah, inji manzon Allah (saw):*

*_"من قال لا إله إلا الله ابتغاء وجه الله، ختم له بها دخل الجنة، ومن صام يوما ابتغاء وجه الله ختم له بها، ومن تصدق بصدقة ابتغاء وجه الله ختم له بها دخل الجنة"_*

*_"Duk wanda ya ce La Ilaha Illal-Lah don neman yardar Allah, kuma ya mutu da ita zai shiga Al-Jannah, haka duk wanda yayi azumin don nemar yardar Allah, kuma ya mutu dashi zai shiga Al-Jannah, da kuma duk wanda yayi sadaka don neman yardar Allah zai shiga Al-Jannah"_*

20. *_"Allah ya tanadi  kololuwar Al-Jannah ga masu Azumi yadda Shari'ah ta tanadar, da kuma masu Ciyarwa, da masu magana mai Taushi ma yan'uwansu, da masu yada sallama tsakanin jama'ah, da masu sallah lokacin da mutane ke barci*

*Duk wadan nan sun zo a Hadith na manzon Allah kamar haka:*

*_"إن في الجنة غرفا، يرى ظاهرها من باطنها، و باطنها من ظاهر، أعدها الله تعالى لمن أطعم الطعام، وألان الكلام، و تابع الصيام، وأفشى السلام، وصل بالليل والناس نيام"_*

*_"Lallai cikin Al-Jannah akwai manyan Gini na dakuna, daga ciki kana ganin waje, daga waje kana ganin ciki, Allah ya tanadesu ne ga masu ciyar wa, da masu iya magana mai taushi, da masu Azumi da masu Yada sallama(ga wanda suka sani ko wanda basu sani ba) da masu Sallah cikin dare mutane na barci"_*

21. *Allah na karban addu'ar mai Azumi har lokacin da zai sha ruwa, ba a mayar da addu'arsa baya. Hakan ya fito ne daga baki fiyeyyen Halitta manzon Allah (saw) yadda ya ce:*

*_"ثلاثة لا ترد دعوتهم: الإمام العادل، الصائم حتى يفطر، ودعوة المظلوم يرفعها الله فوق الغمام يفتح لها أبواب السماء، ويقول الرب: بعزتي لأنصرنك ولو بعد حين"_*

*_" (mutane nau'uka) uku ba'a mayar da addu'arsu: Shugaba mai adalci, mai Azumi har yasa ruwa,  da addu'ar wanda aka zalunta, Allah zai daga ta har zuwa Girgije san nan a bude mata kofofin Sama, Ubangiji sai ya ce : Na rantse da buwayata sai na taimakeka ko da bayan shekara ne"_*

   *Allah yasa da wan nan yar nasiha ta zamu amfana baki daya, Allah ya kara bamu ladansa Ameeeeeeeeeeeen*

——N.B.——
*U CAN SHARE THIS FISABILIL-LAH*
——————

Via
*hdindima.blogspot.com*

RAMADAN MUBARAK (09)

*MARABA DA BABBAN BAKO RAMADAN*

🌿🌿🌿🌿🌿🌿
🌿🌿 *0009*🌿🌿
————————
*By Haruna I Muh'd*
*08069582878*
*hdindima.blogspot.com*

———————
*FALALAR AZUMI*
———(F)———

16. *al-Qur'an da Azumi zasu ceci masu yinsu ranar al-Qiyamah kamar yadda manzon Allah ya fada:*

*_"الصيام والقرآن يشفعان للعبد يوم القيامة، يقول الصيام: أي يا رب منعته الطعام والشهوات بالنهار، فشفعني فيه، ويقول القرءان: منعته النوم بالليل، فشفعني فيه"_*

*_"Azumi da al-Qur'an za su ceci bawa ranar al-Qiyamah, Azumi zai ce: Ai ya Ubangiji na hanashi cin abinci da wasu Sha'awarsa da rana, Allah ka bani cetonsa, Sallah ma zai ce: Ya Ubangiji na hanashi barci cikin dare (yana Sallah): Allah ka bani cetonsa"_*

17. *Azumi na gusar da Kullace-kullacen wani ko wasiwasi ko yawan fushi. Manxon Allah (swa) ya ce*

*_" صوم شهر الصبر، وثلاثة أيام من كل شهر: يذهبن وحر الصدر"_*


*_"Azumi na wata guda sai da hakuri, da kuma azumin da ake yi Uku a ko wani wata, suna gusar da kyashi(kofe ko takaicin) a cikin zuciya"_*

18. *Azumi kofa ce daga kofofin al-khairi, kamar yadda manzon Allah (saw) ya ce:*

*_"الصوم جنة، والصدقة تطفئ الخطيئة كما تطفئ الماء النار، وصلاة الرجل من جوف الليل....."_*

*_"Azumi garkuwa ce, Sadaqa kuma tana kankare kura-kurai kamar yadda ruwa ke kashe wuta haka ma sallar mutum a cikin tsakiyar dare*_*

   *Allah yasa da wan nan yar nasiha ta zamu amfana baki daya, Allah ya kara bamu ladansa Ameeeeeeeeeeeen*

——N.B.——
*U CAN SHARE THIS FISABILIL-LAH*
——————

Via
*hdindima.blogspot.com*