Wednesday, 7 June 2017

RAMADAN MUBARAK (11)

*MARABA DA BABBAN BAKO RAMADAN*

🌿🌿🌿🌿🌿🌿
🌿🌿 *0011*🌿🌿
————————
*By Haruna I Muh'd*
*08069582878*
*hdindima.blogspot.com*

*———————*
*_ABUN DA MAI AZUMI AKE SO YAYI KENAN NA SUNNONIN MANZON ALLAH (SAW)_*
*———(A)———*

*Assalamu Alaikum*

   *Yan'uwana musulmai a cikin azumi akwai sunnonin manzon Allah da dama da ake son ko wani mai azumi ya dinga yinsu, ga kadan daga ciki kamar haka:*

*1* *Gaggauta shan ruwa da zarar an tabbatar rana ta fadi*

*Manzon Allah (saw) ya ce:*

*_"لا يزال الناس بخير ما أجلوا الفطر"_*

*_"Mutane ba zasu gushe ba suna tare da al-khairi, matukar suna gaggauta shan ruwa"_*

*2* *Fara bude-baki da danyen kayan itatuwa ko dabino ko ruwa*

*_"Sahabin manzon Allah Anas (ra) ya ce manzon Allah ya kasance yana bude-baki da danyen abu, in babu ko da dabino ko da ruwa"_*

*3* *Yin addu'a lokacin bude baki*

*Sahabin manzon Allah, Abdul-Lahi ibn Umar ya ce manzon Allah in yazo bude-baki yakan karanta wan nan addu'a kamar haka:*

*ADDU'AR BUDE-BAKI(SHAN RUWA)*

*_"ذهب الظمأ وابتلت العروق وثبت الأجر إن شاء الله"_*

*_"Zhabaz-Zhama'u, Wabtallatil-Uruqu, Wathabatal-Ajru insha Allah"_*

   *Allah yasa da wan nan yar nasiha ta zamu amfana baki daya, Allah ya kara bamu ladansa Ameeeeeeeeeeeen*

——N.B.——
*U CAN SHARE THIS FISABILIL-LAH*
——————

Via
*hdindima.blogspot.com*

No comments:

Post a Comment