Wednesday, 15 June 2022

WANDA YA HUTA DA WANDA AKA HUTA DA SHI

*🕹️AL-MAR'A ASSALIHA (ZAUREN MACE TA GARI)🤱*

_*مَا الْمُسْتَرِيحُ وَالْمُسْتَرَاحُ مِنْهُ ؟*_
_*🍽️WANDA YA HUTA DA WANDA AKA HUTA DA SHI🍽️*_

✍️ Haruna Isah Muh'd
hdindima@gmail.com

Ka san wanda ake ce masa dan hutu kuwa? Ko kasan wahalalle?

An karbo Hadith daga abu Qatada dan Rib'iy mutumin Madina (RA) ya ba da labari cewa Manzon Allah (saw) ya kasance yana zaune sai aka wuce da wata gawa, sai Ya ce:

_*"Dan hutu ko an huta dashi (wahalalle), sai suka ce (Sahabbai), ya Manzon Allah, wa ne ne dan hutu da kuma wanda aka huta dashi? Sai ya ce bawan da mumini ya huta daga wahalar da cutarwa Duniya, da ya koma zuwa ga Rahamar Allah, amma bawan da yake Fajiri (Dan Iska) mutane, gari guda, bishiyoyi da dabbobi duk suna hutawa da rabuwa dashi"*_

⭕ عَنْ أَبِي قَتَادَةَ بْنِ رِبْعِيٍّ الْأَنْصَارِيِّ رَضِيَ اللَّهُ عَنْهُ ، أَنَّهُ كَانَ يُحَدِّثُ أَنَّ رَسُولَ اللَّهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ مُرَّ عَلَيْهِ بِجِنَازَةٍ، فَقَالَ :

*▪️مُسْتَرِيحٌ، وَمُسْتَرَاحٌ مِنْهُ . قَالُوا : يَا رَسُولَ اللَّهِ، مَا الْمُسْتَرِيحُ وَالْمُسْتَرَاحُ مِنْهُ ؟ . قَالَ : الْعَبْدُ الْمُؤْمِنُ يَسْتَرِيحُ مِنْ نَصَبِ الدُّنْيَا وَأَذَاهَا إِلَى رَحْمَةِ اللَّهِ، وَالْعَبْدُ الْفَاجِرُ يَسْتَرِيحُ مِنْهُ الْعِبَادُ وَالْبِلَادُ وَالشَّجَرُ وَالدَّوَابُّ▪️*

📚 صحيح البخاري (6512)
*ــــــــــــ*

*🌟KARIN BAYANI🌟*
*➖Duniya gonar Lahira ce, a cikin ta ne mutane ke girban ayyukansu* wanda ya yi Alkhairi Ya samu Alkhairi, wanda ya yi sharri ya samu Sharri!. A lahira akwai sakamako imma al-Jannah ko Wuta mai tarin musiba da wahala da  kuma har abada ne.

A cikin hadith din nan akwai nuna mana ashe kowa na karkashin abu biyu ne, ko dai dan al-Jannah ko dan wuta, tun daga mutuwa mutum ke gane hakan.

*📜شرح الحديث📜*

*💡الدُّنيا مزرعةُ الآخِرةِ يحصُد فيها الناسُ ثِمارَ أعمالِهمْ،* إنْ خيرًا فخيرٌ وإنْ شرًّا فشرٌّ، وفي الآخِرةِ يكونُ الجزاءُ إمَّا إلى جنَّةٍ وفيها الراحةُ الأبدِيَّةُ، أو إِلى نارٍ وفيها التَّعبُ والنَّصَب والشَّقاءُ، وفي هذا الحَديثِ يَحكي أبو قتادةَ الأنصاريُّ رضي الله عنه: *"أنَّ رسولَ الله صلَّى الله عليه وسلَّم مُرَّ عليه بجَنازةٍ"،* أي: مرَّت عليه جنازةُ ميِّتٍ محمولةٌ لتُدفَنَ، فقالَ: *«مُستَريحٌ ومُستَراحٌ مِنهُ»،* أي: إنَّ الجنائزِ والأمواتِ عندَ انتِهاءِ آجالِهِم بينَ حَالين: إمَّا أنْ يستَرِيحَ الميِّتُ، وإمَّا أن يستريحَ الناسُ من الميِّتِ. فقالَ الناسُ: *"يا رسولَ الله، ما المُستَريحُ والمُستَراحُ مِنهُ؟ قالَ: العَبْدُ المؤْمِنُ يَسترِيحُ مِنْ نَصَبِ الدُّنيا وأذَاها إلى رَحْمَةِ اللهِ"،* أي: يَستَريحُ العبدُ المؤمنُ بعدَ موْتِهِ منْ تَعبِ الدنيا وأذاها بدُخولِه في رحمةِ اللهِ ورِضْوانِه، فيَنْتَقِلُ من حالِ التعبِ إلى حالِ الراحةِ.
 
*▪️ DARUSA*

_*⚓1. Ashe in mutum ya zama bata gari, kowa na cutuwa dashi, har Allah ya hana mutane arziki, a rasha ruwan sama, a rasa dabbobi a rasa bishiyoyi!*_

*💡وأمَّا العبدُ الفاجرُ، وهوَ العاصي أو الكافرُ،* فيَستَريحُ منهُ العِبادُ والبلادُ، والشجَرُ والدَّوابُّ أي: يَستَرِيحونَ من فُجُورِه وشُرورِه وأذاه، وهي أفعالٌ تضُرُّ بالعِبادِ، وتكونُ سببًا للهلاكِ لو كثُر الفُجَّارُ، فيَمنَعُ اللهُ الخيرَ والمطرَ فيَهلِكُ جميعُهُم بما فيهِم الشَّجرُ والدَّوابُّ.
 
_*⚓2. ko wani Musulmi Allah ya bashi zabi tun a duniya, ya zabi zama na gari ko akasinsa, dan an sanar dashi komai.*_


*💡وبهذا التَّبيِينِ والتَّوضيحِ النَّبوِيِّ فإنَّ المسلمَ قد وضَعَ أمامَه الاختِيارَ فليَخْترْ لنفْسِهِ ما أحبَّ،* وليعملْ وليجْتَهدْ حتى يكونَ مُستَريحًا في الآخرةِ.
 
_*⚓ 3. An gwada mana yadda mutane zasu kasance a lahira, wasu yan al-Jannah, wasu kuma yan wuta.*_

*💡وفي الحديثِ:* بيانُ أحوالِ الناسِ بعدَ الموتِ فمنهمْ شقيٌّ وسعيدٌ، ومُستريحٌ ومُستراحٌ منهُ.
 
_*⚓4. Cutarwan da Fajiri dan iska yake yi bai tsaya akan Mutane ba , ya shafi bishiyoyi da Dabbobi.*_

*💡وفيه:* بيانُ أنَّ ضررَ الفُجورِ والعِصيانِ يتَجاوَزُ شخصَ الفاجرِ إلى الناسِ والشَّجرِ والدَّوابِّ.

Allah ka samu daga cikin wadan da zasu huta ba wadan da za'a huta dasu ba. Ameeeeen.
*________________________*

No comments:

Post a Comment